Dare da rana
kai ne abin tunani na
Aminci ya
tabbata ga farin cikin zuciya
Bayan gaisuwa
da fatan alkhairi ina gabatar maka da wannan sako ba don komai ba sai don tuna
tarwa a gareka da irin soyayar mu.
Masoyi na, kada
ka manta a dare da rana kai ne abin tunani na, a duk lokacin da nakwanta idan
har ba muryar ka na jiba to faufau ni da bacci munyi ban kwana, yau kimanin
shekara biyu da yan kwanaki kenan da na kamu da sonka amma na kasa na sanar da
kai nayi kokarin nuna alamu amma sai nake ganin kamar baka ma san inda na dosa
ba, Ibrahim ka sani cewa bazan iya rayuwa ba idan ba tare da kai ba,
Ibrahim kai ne kadai zaka iya zamuwa gata a wuri na, shin me yasa zuciya bata
jin rarrashi ne?, ni da kai na na sani Ibrahim ya san irin zafi da kuncin da
mai so kan shiga idan har bai samu gata ba a inda yake nuna soyayyar sa ba.
Ibrahim me yasa idan ina nuna maka kauna da tausayi da kuma kulawa lokacin kake
kauracewa a gareni? Ka da ka manta shi so hallittace kuma jaraba ce kuma baka
sanin lokacin da yake riskuwar ka kamar yanda baka sanin kiskuwar mutuwar ka.
Tunani na ya
yanke basira ta ta dallashe, shawarwari na sun kare, boyon da nake ya kai
karshe yau ne ranar da ta zamu ranar tarihi a wurina. Ina sonka, ina kaunar ka
Ibrahim, bazan taba mantawa da kaiba, ka aminci da ni.
Kaunar ka nake dare da rana
Aisha Abubakar
1. Oyoyo Masoyiya ta
2. Na aminta da ke
3. Kin kasance farin ciki
4. Ina kike mai So na
No comments:
Post a Comment