Monday, 19 March 2018

HUBBUL YAQEEN SERIES 1

Book 1 of Hubbil Yaqeeen Series 

HUBBUL YAKIN
  
ASIYA SADIQ MACCIDO
(ASIKHAN)

Copyright © Asiya Sadiq September, 2017
Hakkin Mallaka (M) Asiya Sadiq September, 2017

Published in Nigeria by
Sharhamak Computer Ventures
Beside Birnin Kebbi Local Government Secretariat
Kebbi State, Nigeria
Website: www.hausacc.ml
Tel: 08113777717

 GODIYA
Godiya ta tabbata ga Allah kuma aminci ya tabbata a bisa za babben jakada shugaban Annabawa Muhammad dan Abdullahi wanda aka saukarwa fiyayyen littafi ma’ana al-kur’ani domin ya zama shiriya da kuma waraka ga muminai, Yar da da aminci su kara tabbata abisa iyalan gidansa da sahabbansa da kuma mabiya tafarkinsa har ya zuwa ranar sakamako.
Ina kara mika godiyata ga Allahu subhanahu wata’ala, wanda shine Ya bani ikon rubuta wannan littafi.
Ina mika godiya ta musamman ga Maihaifana Abubakar Sadiq Maccido da Zainab Sadiq Maccido da Aisha Sadiq Maccido da kuma Rukayya Sadiq Maccido ga irin dawainiyarsu da kuma nuna kulawarsu akaina, fatana Allah Ya biyasu, Ya kuma sanya alhairi a cikin rayuwarsu baki daya amin.
Godiya ta ba zata kare ba har sai na mikata ga yan uwa da aminai na kamarsu: Farida M. Bello, Shamsudeen Sadiq Maccido, Sharahbil Muhammad Sani, Yakub Al’amin Yakub, Walid Kabir Gada, Malam Usman Umar Aliyu, Badadiya, Habiba, Balki, Maryam Mufida, Ummu, Baby, Billy, Sumayya, Fatima, Jamila da kuma Lubabatu da fatar Allah Ya sanya alhairi a cikin rayuwarmu baki daya amin.

HUBBUL YAKIN
Misalin karfe biyar da rabi ne na yamma, a daidai lokacin da ake tashi daga islamiya, dalibbai daga ko ina sa bullowa sukeyi kowa yana kokarin ya koma a gida .Wata natsatstsuwar yarinya mai hankali da kamala ce sanye da uniform dinta na islamiya hijab dogo har kasa tafe take tana tako a hankali kamar wadda kwai ya fashewa a cikin uniform din sky blue ne sunyi matukar yi mata kyau duk da ba wani kwalliya tayi ba, domin ga dukkan alamu ita irin wayannan ne da ake kira da “Natural beuties” Ma’ana (wayanda  basa bukatar kwalliya) domin wai ta kara musu kyau. Bakowa bace wanna face Bilkisu mai gadon zinari ‘ya daya tilo a wurin Malam Iro. Yau gabaki daya a cikin wani yanayi take jin kanta kuma itama kanta ta kasa gano meke damunta, kawarta Asiya ba karamar gwagwarmaya ta sha akan dai ta ga ta sake ta dawo dai- dai kamar yadda aka saba amma abin yaci tura, ga baki daya komai ba yayi mata dadi a duniya, kuma ta rasa gano dalilin faruwar hakan, bata tsaya fira da Asiya ba da aka tashi sakamakon tsayar da ita da Malam Babba ya yi, kawai sa kai tayi gaba abinta. A daidai wurin wani mazauni ta tsaya ta gaida dattawan da ke wurin cikin girmamawa, ansawa sukayi ga baki dayansu, yauwa Balkisu dama ke nake jira ungo wannan ledar kaiwa Umman ki, wani dattijo wanda ko ba’a  gaya maka ba kasan  mahaifintane akan tsananin kamar da suka yi, ya fada tare da mika mata ladar, hannu biyu tasa ta karba batare da tace komai ba, tasa kai tayi gaba.Wani daga cikin dattijawan wanda tun sa’adda Balkisu take wurin yake kallonta yana murmushi, shine ya bita da kallo har sai da ta kure masa.Ajiyar zuciya yayi sannan ya fara Magana gaskiya Mallam Iro kayi dacen diya maihankali da natsuwa ga ganin girman manya, murmushi mahaifin nata yayi mai nuna alamar har a cikin ranshi yaji dadin abinda ya fada ba tareda ya fadi komai ba. Gabaki dayan dattawan wurin kowa ya amsa da cewa ai kuwa gaskiyar ka Bilkisu yarinya ce mai hankali, Malam iro ya katse zancen tare da fadin ai kaima Alhaji Haliru ba karamin dace kayi ba da samun yaro mai natsuwa ga hankali da kokari, a gaskiya duk afadin anguwarnan ba sa’an Sulaima dana sani da yayi hankalin shi da sanin ya kamata.Ai kuwa ka tunamin ina zuci-zucin na gaya maku amma sai na manta, inji Alhaji Haliru ga baki daya hankali ya koma kanshi, me ya faru? Wasu mutum biyu suka hada baki.Sulaiman ya samu aiki Kaduna, kunsan ya tura takardar neman aiki, jiya sunanshi ya fito ya samu aiki a Kaduna, an bashi nan da wata hudu masu zuwa da yakoma ba kin aiki Insha Allah.Masha Allah! ai kuwa wallahi munyi murna Allah ya sanya Alkhairi ga baki dayan mutane suka ce  Ameen, Alhaji Haliru ya fada tare da dan ya mutsa fuska kamar wanda ya tuna da wani abin haushi.Kunsan meye damuwata? A hakikanin gaskiya bana so Sulaiman yayi wannan tafiya shi kadai, har Kaduna garin da bayada kowa sai Allah ni na ma rasa me yasa aka kaishi aiki can, hakane to amma kuma ai namiji ne wanna ai ba abin damuwa bane ni a  gurina. Wani daga cikin mutanen ya fada. Ba wannan nake nufi ba, ina nufin zaifi dacewa da ace yanada mata kaga sai kawai su tafi tare abinsu ai kaga zata ringa dabe masa kewa ko? A gaskiya kayi tunani Alhaji, ta mai zai hana  ayi masa aure ne yanzu sai kawai ya  wuce da Amaryar tasa? Aikai Malam Sani ba auren bane bana so nayi masa a’a Inaso ne na samar masa mace mai hankali da natsuwa. Abu mai sauki ai ina ga ga Bilkisu nan kamar halayansu yazo daya, me zai hana sai a hada su ko kuwa? Malam iro ne ya fadi haka kai tsaye tare da jefawa Alhaji Haliru wani kallo mai nuna alamar ko kuwa ya ka gani? Kamar ya san abinda yake zuciyar Alhaji Haliru kenan, shi tun da can yana son ace Bilkisu ta kasance suruka a gareshi, a ganin shi ba wanda ya dace ta aura face danshi Sulaiman. Da hanzari ya amsa da wallahi kuwa da gaskiyarka malam Iro wannan abin da ka fada shine daidai, Alhamdulillahi kai! da kuwa abu yayi daidai wallahi. Kai masha Allah a hakikanin gaskiya kunyi tunani yanzu sai arufe zance guda, Malam Iro ne ya fara da cewa ya mallakawa Sulaiman “da” a wurin Alhaji Haliru “yar” sa Bilkisu, shi kuwa Alhaji ya karba hannu bibbiyu tare da bashi sulaiman din damar yazo a gidansa domin su dai-dai ta a tsakaninsu kafin ranar daurin auren ta zo.Murna a wurin Ahaji Haliru ba’a cewa komai, kamar ma shine angon. Bai jira lokacin tashi yayi ba ya hauri takalmansa ya nufi gida cikin farinciki kamar wani wanda aka yiwa albishirin shiga aljanna. Shima Malam Iro da saurin sa ya nufi gidansa bayan an tashi daga mazauna, Allah-Allah ya ke yi ya isa gida, ya gayawa matarshi labari mai dadi har a ranshi yasan Sulaiman yaro ne mai hankaali da sanin ya kamata yana kuma sane da cewa zaya rike masa diyarsa da amana. Tun a kofar gida ya fara rangada sallama har ya isa a cikin gidan, da hanzari uwargidan shi ta fito, sannu da zuwa maigida an dawo lafiya, lafiya kalau  ina Bilkisu? Yanzunnan taje raka kaawarta Asiya, lafiya dai Baban balarabe   naga sai wani faman far’a kakeyi ko tsintuwa jakar kudi kayine ta fada cikin zolaya, murmushi yayi hade da yin gajeren tsaki,wannan abin yafi  tsintuwar jakar kudi, to madallah bari na dauko tabarma naji wannan abin  wani irin abin alkhairi ne haka,har ta dan yunkura ya dakatar da ita, ki bar tabarma kawai lokacin sallah ya gaba to yanzu masallaci zan wuce, gyara tsayuwarta taayi   ta fuskance shi da kyau ina jinka baban Balarabe. Wato wani abin alkhairi ya same mu, kinsan Sulaiman dan gidan Alhaji Haliru na can hayin kusa da masallacin jumua’a? eh! Da hanzari ta fada tana kallon shi, mahaifinshi ya nemar masa auren Bilkisu kafin zuwa nan da wata hudu za’ayi biki a kai amarya dakinta. Daga nan ya kwance mata biri har wutsiya yanda sukayi a mazauna. Itama fara’ar takeyi ta kuma yi na’am da maraba da zancen, sai dai a wata zuciyar tana jin tausayin Bilkisu ne, ta yaya za’ayi mata haka kuma wai duka abin cikin wata hudu, bama wannan yafi damunta ba wai ba anan cikin garin zasu zauna ba a’a har Kaduna, inda su dukan su ba mai dangin iya balle na baba. Arwala yayi ya wuce masallaci tareda gaya mata bazai samu dawowa da wuri ba zasuje wani wuri kuma zasu dan dade yasa kai ya fita, da hanzari ya dawo da baya yauwa Hauwa’u ki fa gayawa Bilkisu komai idan ta dawo kinji! Tau ta fada tare da daga kai alamar naji. Yasa kai ya fita, daukar butar daya gama alwala tayi ta fara yin alwalar itama, har a cikin ranta tana farin cikin da abinda maigidanta ya gayamata kuma tasan bazai cutar da diyar shi ba. Sai dai kawai bata san ya Bilkisu zata dauki al’amarinba duk da tasan baza taki yin abin da mahaifinta yace tayi ba. Kamar ta tuna da wani abu kuma sai kawai ta shararda wannan zancen ta fara murna a ranta tana hango yar tata a matsayin amarya. Kabbarta sallar ta keda wuya sai ga Bilkisun ta shigo, ta nemi guri ta zauna a falo, remot ta dauka ta fara canja tasha daga NTA Hausa zuwa zee cinema, wani film akeyi duka hankalinta yana a wurin. Bayan mahaifiyar tata, ta idar da salla ta juya ta fuskance ta, tadan jima tana kallon nata batare da ita Bilkisu ta gani ba, kasantuwar duka hankalinta yana kan abinda take kallo, sai da ta kira sunan ta sannan ta waigo, Umma kin kare sallar ashe, ina wuni, lafiya kalau mi ya tsai dake daga rakiya? Wallahi Umma Asiya ce ke bani labari bamu san lokaci yana tafiya ba kuma sai akayi daidai da mu dukan din ba mai yi shi yasa bamu damu ba mukaci gaba, daga kai kawai tayi sai da tayi dan shiru na mintoci sannan ta fara da cewa: Maigado (sunan da take kiranta dashi kenan) duk da yake ba it ace yar fariba kasantuwar duk yaranda ta Haifa rasuwa sukeyi Bilkisu kadai Allah ya raya musu. Itama Bilkisu ta fuskanci mahaifiyar tata tace na’am Umma, dazu mahaifinki yazo yayi min wani albishir wanda naji dadin shi sosai. Ya kuma umurceni dana gaya miki wannan abin alkhairin. Gabanta taji ya fadi batareda tasan dalilin ba murmushin yake tayi meye umma, wani abin alkhairi ya same mu? Eh maigado babanki ne ya zabar miki da mijin aure, yaro mai hankali da natsuwa kyakawa dashi, har ma angama Magana za’ayi bikin ku cikin wata hudu masu zuwa. Kamar saukar aradu taji abin, shin wai ko mafarki ne takejin wannan, ko kuwa zolayace Umma keyi mata? Kuma tasan Umma bata haka da ita, hakikanin gaskiya dai take gaya mata,da kyar ta hadeye yawu, tace aure fa kikace Umma, eeh aure mana maigado.ya naga kamar bakiji dadin abinda na fada  ba, maigado ki sani cewa mu iyayenkine  ba kuwa  zamu zabar miki abin da zai cutar da ke ba, anan ta dukufa  tana maiyi mata nasiha tareda lurarda ita, har aka kira sallar isha’I, ta miko da nufin kabbarta sallah dan juyowa tayi a dai-dai lokacinda Bilkisun itama ta mike ta nufi dakin ta.Maigado ta kirata tana murmushi, waigowa tayi na’am Umma,ba za ki tambayi ko waye surukinnawa ba? Dukar da kanta kawai tayi, murmushi mahaifiyarta ta sakeyi, sulaiman na can hayin gidan da yake kusa da masallacin Jumuah, dan maman sule ta idar da maganarta da yar gajeruwar dariya, ita kuwa Bilkisu da hanzari ta fice daga falon ta fada dakin ta, a hankali ta zauna kan gadonta a dai-dai lokacin da ta kwanta tabi gadon, fankar take kallo amma ga baki daya halinta baya wurin, ji take kamar wata almara, wai ita za’ayiwa aure cikin wata hudu. hoton sulaiman h ta gani a’a idunuwanta a gaskiya tasan Sulaiman baya da matsala kuma yana da halaye masu kyau amma kuma batajin son shi kona kwayar zarra a ranta, dolene tayi biyayya ga mahaifanta domin ita kanta tasan samun miji irin Suleiman ba karamar sa’a bace amma ya zatayi ita dai ba sonshi bane batayi kawai dai tayi alkawalin ba zata sake son wani da namiji ba har karshen rayuwarta. Rufe idanunta tayi to idan ma bata amince da Sulaiman dinba wa take dashi da take so.kwatsam  masoyinta rabin jikinta ya fado mata a rai wato Usman wanda take kira da (MAN) wani hadadden saurayi ne wankan tarwatsa sosai yana da jiki amma daidai dashi, yana da  manyan idanu farare  tas kamar madara, hancin sa irin wannan ne da yake faro tsawon shi tun a saman goshi wato dai irin na shuhrakan, yana dauke da wushirya da take haskaka fararen hakuransa kyau idan yayi dariya, kai a hakikanin gaskiya duk inda haduwata ta kai Usman ya wuce can domin idan ka ganshi ba tare dayayi Magana ba zaka zaci irin yan indiyan nan  ne dake zuwa kasashe-kasashe yawon bude ido, sun hadu ne da Bilkisu lokacin tana (Secondary School SS1), hakika Usman gwanine wurin iya soyayya, sun kasance suna son junansa so na hakika Usman shine saurayin Bilkisu na farko a duniya  tun tana SS1,suke tare har takai SS2, Suna matukar son junansu kamar su hadiye kansu amma ba wanda ya sani a gidansu kai karewa ma ko Aminiyarta bata sani ba duk kuwa irin  shakuwar da suka yi a duniya. Wata ranar litinin bayan an tashi daga makaranta fitowarta bakin (Gate) din ta hangoshi tsaye cikin wani mawuyacin hali da hanzarinshi yazo ya taryeta suka hadu, a inda suka saba haduwa ya nufa.Lafiya (MAN) naga kamar kana cikin damuwa meke faruwa? Sai da yayi ajiyar zuciya sannan ya fara BILLY (shine sunanta yake kiranta dashi) nazone muyi------- kasa idarwa yayi idanuwansa suka cika da kwallah, muyi me (MAN) don Allah ka gayamin hankalinta duk atashe. BILLY nazo ne muyi bankwana zanyi tafiya kuma zan dan dade ban dawo ba, yanzu ma ni kadai ake jira a wuce.Nan take idanuwanta suka cika da kwalla, idan ka tafi yaushe zaka dawo ne? Ta fada dai-dai lokacin da hawayanda ke makale idanuwanta suka kwaranyo. Wani dogon nunfashi yayi tare da kanne nashi hawye bazan dade ba BILLY zandawo komai daren dadewa, zan dawo gareki domin ke kadai ce matata a duk fadin duniya nan kamar yanda nine kadai mijinki, karar wayarshi yaji wadda ke cikin aljihunshi, bai kula ba, ya cigaba da jawabinsa, “Nayi miki alkawarin duk fadin duniyar nan ba wadda zanso idan bake ba, zan dawo muyi aure dake mu zauna har karshen rayuwar mu”.  Duk iya daurewar da ya yi a wannan karon sai da hawaye suka zuba a idanuwansa. Ita kuwa Bilkisu dama ta ke yi, juyawa ya yi da karfi “BILLY sai wata rana!” bai sake waigo inda ta ke a tsaye ba. Tafiya kawai yake, hawaye na zubar masa kamar wanda ya rasa iyayensa ko aka gayawa bazai sake ganin taba har abada. Bilkisu durkushewa ta yi a kasa tana kuka tana kiran sunansa. Tun daga wannan rana bata karajin ko labarinsa ba, abin da yafi ma ta zafi da radadi a zuciya shine bata da hotonsa ko guda daya wanda zata rika dubawa tana tunawa dashi sabanin shi da ya ke da hotunta bila adadin, domin kuwa ko haduwa suka yi suna hira zai rika daukanta hotuna ba adadi, kuma duk lokancin da tayi hotuna sai ta bashi. Wani tsaki ta saka mai dauke da takaici, “Mwts” a dai-dai lokacin da ta dawo daga kogon tunanin da ta ke yi, duk fuskarta ta jike da hawaye. “A hakikanin gaskiya Usman bai kyauta ba, haka ma zuciyata bata kasance mai adalci ba da ta kasa mantawa da Usman". Balkisu ke fadar haka a cikin zuciyarta. Wannan shine dalilin Bilkisu da yasa tun daga Usman bata sake gwada soyayya da kowa ba duk da tururuwar masoyan da suka mata zarya, domin irin kyanta da kirarta ta wuce gaban namiji ya kalleta sau daya ba tare da ya maimaita kallon nata ba. Bilkisu farace amma ba tasba, ta na da manyan Idauwa masu (Shape) din nan da ko ba’a sanya musu kwalli ba sai ka zata ai su na da. Ta na da Girar Ido irin dara-daran nan masutsawo da basa bukatar (mascara) wurin bayyana tsabar kyansu, girar idanuwawanta kuma irin bakar nan ce kirin mai matukar sha’awa, hancinta kuwa dogo ne shigen irin na Rani Muhurji shi baiyi tsawo sosai ba amma kuma dogo ne, gashin kanta kuwa dogo ne wanda ya zuba har a gadon  bayanta baki wulik dashi kamar kullum tana saka mishi man da zai kara mishi baki, tanada fararen hakora sai kace sai da aka sanya ruler wajen daidaita su, shape dinta kuwa ko Nicki Minaj sai dai ta bawa kanta lafiya domin kuwa koda ita Bilkisun aka bawa dammar ta kera kanta da kanta iya shape dinda zata yiwa kanta kenan, kai! A gaskiya tsayawa bayanin halittar da Allah yayiwa Bilkisu bannan lokaci ne domin kuwa sai mu cika rabin littafi muna bayani ba tareda mun kammala ba. 
Zamu cigaba Insha Allahu

No comments:

Post a Comment