SANADIN SO
Ni na aminta so zai sakani in miki komai
Na zamo gwani na fada kan sonki an kirani jarmai
Soyayya silar rikirewata na rike makamai
Sunanki ya zamo lakabi agareni na zama na sadiya fadamai
Naga sauyin al’amarina
Sai tunani safe da rana
Duk wanda za ya so ki nashaida ba za ya kai ya ni ba
Sunanki ya fimin komai daraja ban gano ya shi ba
Wazai tabaki in har gani da rai bai ciyo wuyaba
Sam bani fargaba sanadin soyayya na daura danba
Ban bukatar amini gyara
A tabaki in saka sara
Shi so saboda bashi da tabbas ne aka kirashi tsuntsu
Hanta da zuci in sunka firgice so ne yake tsumasu
Zanso batun da nayyo miki masoyiyatawa ki gamsu
Kudade na adana dominki ne nayyi asusu
So yasa na zama gwarzo
Ki ci nama ni inci kanzo
Indai ban ganta ba kunci kan hanani bacci
Ko yannayi na sanyi sai na rika mafeci
Kanne gareta in har na gansu sai na basu tukuici
Ko don su bani labarin abin kauna na bar maraici
Sannan rai yay ta nishadi
Su fadamin don naji dadi
Dukkan abokanai na sukan fadamin inbi a sannu
Nan take ince musu munafukai sun sakan idanu
Bana tsoron nayiwa mutum rauni ko na balla hannu
Nazam abin ayo rarrashi sai dai abini sannu
Ba a son raina na zamo ba
So ne ya sakani ukuba
Karko guda nai adduar iyaye taimini rana
Badan haka ba da tuni naje kas ba a kara jina
Kango da na shige makami nake boyo kuji batuna
Ko da wani zai kawo latsi gun rabin jikina
Makami sai da na dakko
Ban tsoron ai mini tarko
Ko yan sanda na zam musu tsawon gari sun gaji da nema
Ba mugun furuci na iyaye kaina na ga alama
Burin mahaifiyata na shiryo zuciya tayi salama
Na sari saurayi ga budurwa ta sanarwa hukuma
A gida namu na bar kwana
Banso ku gano laifina
Duk wadda nai hakan domin ta ashe bata san dani ba
Nasa yayanta yayi fada mata wai duk bata zataba
Ko zata makaranta a baya zan bita bada wai ba
Na hankure da tawa school din sai dai ingararamba
Indai na rikice ita dauce ke saita lammarina
Indai tana fadamini zan bi ko babu ra’ayina
Yau gani da damuwa ni da ita zanso ace mu gana
Amma a yanzu na kasa in fada mata sirrin cikina
Wayyo ni Allah Kaina
So ya canjan kudurina
Daure ki soni zan canja rayuwata tayo nagarta
In baki soni ba daga kai naki ban kara kula mata
Inkin aminta zaniyo sujuda domin ko nayi rata
Fatan da nai abin so gareni kada kimin mugunta
In kikai haka kin mini gata
Addata zai ajiye ta
Zakuji a kashi nabiyu sahiba ta me ta fadamin
Nan gun ne ni zan barku
Sharha M.S Nuhu Naku
No comments:
Post a Comment