HUBBUL YAKIN cigaba
ASIYA SADIQ MACCIDO
(ASIKHAN)
Copyright © Asiya Sadiq September, 2017
Hakkin Mallaka (M) Asiya Sadiq September, 2017
Published in Nigeria by
Sharhamak Computer Ventures
Beside Birnin Kebbi Local Government Secretariat
Kebbi State, Nigeria
Tel: 08113777717
Book 1 of Hubbul Yaqeeen Series |
Shi kuwa
Sulaiman tunda ya wuce bai tsaya ko inaba sai a bakin gate din office dinsu,
kaf ya tsaya tsam kamar wanda yaga wani dodo, sani ya manta oganshi yayi
tafiya, ya tafi wajen wani comfrence da za’ayi a sokoto kuma zasuyi kamar kwana
shida zuwa biyar basu dawo ba, to meyasa ma wai bai tuna ba sai a yanzu, wani
tsaki yayi mai hade da takaici, said a yayi kamar minti biyar a bakin gate din
office din nasu sanna ya tada mashin dinshi ya nufi gidan Alhaji day a basu
haya domin ayita takare idan yanada wani gida ya canza musu ko kuwa asan yanda za’ayi
kafin nan da zuwan kwanaki shida da oganshi zai dawo ya nemi transfer ya bar
gari tun a kan layin gidan Alhajin ya fara ganin dandazon mutane ba adadi har
ya iso kofar gidansa, me zai gani ga dukan alamu wani abu akayi ras! Gabansa ya
fadi a wurinda shimfida take ya dire takalma yayi sallama ya mike hannu tabbas
gaisuwar rasuwa ake yayi gaisawa aka ansa masa ya nemi ya gana da babban dansa,
kasan cewar yasan sulaiman domin tare dashi akayi process din gidansu Sulaiman.
Bayan da Sulaiman ya kara yi masa gaisuwa ya tambayeshi yanda haka ta faru, ya
shaida mai matukar rudarwa, a jiya da dare ne yana bacci sai kawai akaga ya
mike tsaye ya sauka daga kan gado, ya farayin da baya-dabaya yana ta ko’ina har
ya fadi kasa, likitoci sun auna sun fada cewa sakamakon ganin wani mummunan tashin
hankali da idon dan adam da kuma kwakwakwar sa basa iya dauka da yayi shiya
hifar masa da wani matsanancin bugun zuciya da har yayi sanadiyar rasa
rayuwarsa a nan take dirshan ya fadi a kasa hawaye suka riqa zuba a idanuwansa,
al’amarinda yayi matukar bawa mutanenda ke wurin mamaki kenan hade da tausayin
musamman babban dan Alhaji, lallashin shi aka dingayi har ya dawo cikin
hankalishi ya daina kukan da yake. Shi kadai yasan abinda yakewa kuka tabbas
shakkah babu akwai wani mummunan abu dake shirin faruwa dasu, gashi sub a yan
gari ba yaya zai yi. Ya zabura ya mike ya sake gaisuwa yayi sallama ya wuce,
dole subar garinan gobe-gobe ba domin sko yanzu lokaci ya kure musu bad a sun
bar garin a yau, kara gudu yayi kamar wanda zai tashi sama domin kar dai wani
abu yazo ya sameta domin kuwa Bilkisu shi c eta fado mishi a rai, kar dai wani
abu yazo ya sameta. Krar shit ta dawo masa da hankalin shi daga tunaninda
yakeyi bai yi ni yar ya dauka ba kuma dai yaji bari ya dauka aljihu ya zara wayar
shi sanan abakinshi Nuhu ya gani da sauri ya dayka ya karakan kunnensa, slamu
alaikum ya fadawa alaikussalam, Sulaiman don Allah kayi hakuri kaga ban samu
dammar kawo su uUmmi ba Wallahi jiya da sakiyar dare mamansu ta kuma da
matsanancin ciwon ciki amai da gudawa tun sa’annan muna asibiti sai yanzu muka
dawo, yanzu dai Alhamdulillahi ta samu sauki sosai, kayi hakuri fatun sannan
ban masan ida wayana yake ba sai yanzu da muka dawo bare na kiraka na gagayama
bazan samu dammar kawo su ummi ba kasan ya yanda al’amuran suke wallahi tun
sannan bansamu nutsuwa ba sai fa yanzu da kaga na kiraka. Rasa ta cewa yayi can
ya lalibo kalamai yace ai badamuwa Nuhu Allah dai ya bata lafiya ya tashi
kafadarta sai munzo dubata nida Uwargidata tau amen, amee, Sulaiman, When sai
kunzo, sai an jima ya katse wayar. Wani matsanancin gudu yakeyi kamar ranshi
zai fiita ya nufaci gidanshi haiqan dearest!dearest! dearest! Yake fadi kamar
wani mahaukaci, da karfi yasha kwanar gidansi, kicibis! Yayi da wani abin ban
mamaki, Bilkisu ya hango tana fama dariya tana bye-bye da hannunta, kyar ya iso
a gabanta, murmushi tayi ta nufaci inda yake sannu da zuwa ga baki daya ta
jagula masa lissafi zauwa ke dawa kike bye-bye haka? Malam mu shiga daga ciki
ai ko, biye kawai yake da ita, suka shiga cikin gida su waye suka zo wurinki ne
haka, ni fah da farko duk kin tsoratani n zata ko ke kadaice a gidan duk
hankalina ya tashi, wani kallo tayi mai alamar ina ma fushi da kai, eh ai dole
kace haka ai, ta wani shagwabe murya sanna tace stunda kasan Nuhu ya kawo su
Ummi! Shine ka tafi abinka ka shallake, to sune nakewa bye-bye da yazo daukan
su, nayi-nayi ya jiraka amma yaki ta, su ummi!! Kuma Nuhun ne yazo daukan su!!
Mikewa yayi inna lillahi wa inna illaihi
raji’un, a firgice itama ta mike hakika sulaiman dinta ba karamar razana yayi
ba to muje na razana a cikin abinda ta fada. Lafiya dearest meya faru meye don
Allah gayamin, Bilkisu tashi ki had kayanki gobe-gobe zamubar garinnan, me ya
faru ka gayamin! Ta daka masa tsawa tana mai zubarda kwallah batareda tasan ma
tayi ba, da kyar ya kwantarda hankalinshi ya zaunarda ita kana ya bayyana mata
duk abinda ya faru tun daga farko har rasuwar Alhaji da rashi lafiyar mata Nuhu
duka ya bayyana mata shiru tayi ta kasa koda motsa dan yatsan ta akan tsananin
firgitarda tayi Bilkisu! Bilkisu! Ga baki daya batajin abinda yake fada, said a
ya wujijigata da karfi sanna ta dawo ayyacinta, Bilkisu karki damu gobe-gobe
zamu bar garinan a’a ba sai na ta fada tana mai fashewa da matsanancin kuka,
a’a Bilkisu ki bari gobe tunda sassafe, a’a ta durkusa kasa ta rike masa
guwayyunsa na rokka don Allah Mubargarin nan a yau din nan, nunfashi ya aje, to
shikenan jeki hado kayanki mu wuce, karki damu sa sauran kayan, idan nazo
karbar transfer letter din azan wuce dasaura, shiga tayi ta tattara kayanta
shima tattara nashi kayan yakeyi, sai a yanzu ta gane lallai wayannan basu
Ummmi bane, bayan da ta zuba maganin sai taga duk sun wani kamar rikice, ta
tuna sanda ta aika amina kitechen ta dauko mata plate sam takasa shiga a
kitchen din, sa yanzu ta fahimci tun lokacinda ta zuba maganin basu sake takawa
daga cikin falon ba. Tsam ta mike tunawa tayi da yanda Ummi ta dauko jug a
cikin feeg wanda ta cika da drinks din kwakwa ta wankada akan kofar fita falon
wanda zata fitar da mutum zuwa ta gane da gangan ta fadi ta zubar da drinks din
don dai kawai su samu su fita. Kamala hada kayan tayi a dai-dai lokacinda shima
y agama kamala nashi muje ko yace ta janyo hijabinta data ajiye kalar kayanda
ta saka tace eh, muje tare suka nufi hanyar fita, tsayawa sulaiman yayi ya
kalli gidan da kyau ya gayda kai ya wuce suka kulle gida sun juya zasu wuce
sukaji an kyalkayale da wata mahaukaciyar dariya, duban juna kawai sukayi ba
tareda sun ce ko kalaba sukaja akwatunansu sai a kan titi suka tsaya, wani mai
a daidaita suka tsayar, garge zaka kaimu, yasa kayansu ya nufaci garge din,
misalign karfe uku da rabi ne narana garin ana tsananin zafi, wurin fifa ya
tsayar day an layin su, jira suke ya dauko musu hannu su wuce, ji tayi kamar
ana girgiza kasa, ruguzum komi na wurin ya fara rusgawa cikin kasa, kuwwa da
hrgowar jama’a kawai kakeji, motuna da baburra sairuguzawa sukeyi kamar an
cilla a dai daita sahu su, sulaiman ya runtuma cikin, caf tasa hannuwanta ta
cafkoshi, wani irin tashin hankali mara misaltuwa ta shiga kuka take tana
hargowa karka tafi ka barni tana rike da hannunshi sauran jikinshi kuwa yana
lib, hannunshi ya fara subuce mata tana mai tsala uwar kuwa tsundum ya fada
yana kiiran sunanta Bilkisu! Bilkisu! Sulaiman ya ingi zata, caraf ta dawo daga
wanna mummunan mafarki zatace ko tunani, ita dai tasan a zahiri taga wannan abu
ya faru, lafiya me kike tunani haka? Sulaiman ya katseta, waige-waige take da
idanuwata cikin mawuyacin hali, ke meye? Meya faru? Jin ta kama hannuwanshi ta
jinike da nata, a jiyar zuciya yayi, karki damu masoyiyata insha Allahu zamu
isa gida lafiya, gobe irin wannan lokacin kina gaban Umma, ya fada yana
zolayata, duk day a kokarin da tayi wajen gani tayi murmushi ta kishingida
dai-dai wajen ‘yanBauchi aka ajiye su, sune passengers na farko da suka fara
loda a motar, bayan an saka masu kaya a mota, suka shiga ciki mota suka zauna
suna jiran zuwan sauran passengers, zaunawar su keda wuya dum! Sukaji ko ina
yayi rufe da wani matsanancin duhu smai tsananin muryoyi sukaji kala-kala ta yadda
ba zasu iya tantance ko murya mace, namiji? Ko kuwa karamin yaro ba. Gargadinsu
a kayi da murya mai kaushi akan suyi gaggawar fita daga cikin motar na su koma
ya zuwa gidansu da suka baro, muddin kuwa sukace zasuyi taurin kai, kuwa zasu
hadu da matsanancin hadarin motar da zatayi sanadin halkar duk wani passenger
da ke a cikin motar, sanna kuma aka wayanda basuji basu gani ba, domin kuwa
driver matarshi ta haihu kwana biyu yayi saura ayi biki, idan sukayi sanadiyar
mutuwar wazai dauki nauyin iyalishi kuwa wanda yake kan gaba a kusa da driver
dan makarantane shi kadai ne namiji a gidan su, mahaifinsa ya rasu mahaifiyarsa
ke wahala wajen ganin ta biya masa kudin makaranta. Ita kuwa wannan matar
‘yaranta duka biyu marayu ne ‘yan uwan mahaifinsu sun kwace musu dukiyarsu,
wajen ‘yan uwanta zataje neman agaji. A haka akaci gaba da lissafo musu ko wane
passenger da abinda yake kunshe dashi duk domin dai so fita daga cikin motar
bayanta aka gama gargadinsu, wayau! Sukaga ko’ina ya yaye, kuma motar da suke
ciki hart a cika da passengers, kamar yadda aka shaida musu haka kuwa suka
gani, duk wayanda aka lissafa musu a motar su da ne ke ciki. Kallon juna sukayi
ba yareda sun samu dammar furta wata kalam ba, wayar direba ce yita wau kara,
dauka yayi tareda sallama, slamu alaikum lafiya kalau wallahi, a’a
alhamdulillahi mun gode Allah, amen, amen, sosa kunnenshi yayi yana ‘yar
dariya, eh saura kwana biyu ma ayi bikin ai ina Allah ya yarda. Dam gabansu
yafadi suka sake duban juna da karfi, tare suka hada baki dakata!! Duk motar
kowa ya jiyo ya ba, ana saka kayane a but da hanzari suka bade murfin motar
suka fito, mun fasa tafiya Sulaiman yace gaywa condester, don Allah kuyi hakuri
wallahi mun fasa tafiyar me kace malam, kamar ya ya kunfasa lafiya wanna aima
maganar banzace, duka mutanen wurin suka taso wasu na bayadda hakuri wasu na
zugawa, anan dai aka samu wani dattijo mai hankali da sanin ya kamata, yace
tunda ai ga wasu passengers nan ba sai kawai su shiga a madadin wayannan ba, ai
wannan abun bai kai na wani dogon bayani ba, sukayi masa godiya suka nemi a
dai-daita sahu suka sake saka kayansu suka nufi gidansu da suka saka baro, suka
bar mutanen garage din kowa tana mamakin wayannan mutane haka, su kadai suka
san dalilin da yasa suka bar motar, ba kuzari mai adai-daita ya sauke su a
kofar gidansu, said a suka yi kamar minti bakwai a tsaye suna kallonn-kallo
sanna Sulaiman ya bude gida suka dunguma a ciki, ga baki daya duniya tayi masu
zafi komai ya kulle musu, sun ma rasa ta inda zasu fara bamai cewa kowa ko
kala, suka isa bakin kofar falo ya saka key a ciki yana kokarin mirdawa ya bude
kofar falon, kiririn,kirin wayar Sulaiman tayi kara su duka suka zabura da
karfi, hannu yakai aljihu ya ciro wayar, sunan mahaifinshi ya gani ya bayyana a
gaban screen din wayar shi, dauka yayi, yayi kokarin boye duk wata damuwar shi,
da ke tattare dahshi, slamu alaikum Abba ina wuni lafiya kalau, lafiya kalau
take, komai Alhamdulillahi, Na’am Abba na nameye ya tambaya yana mai nuna
mutukar mamakinshi a filli kamar a gaban Abban nasa yake, kallonta yayi da
hanzari eh yayi murmushin yake yace amen, har yanzu kallonta yake yi, to amen
baba ehan, ya katse wayar har yanzu kallonta yakeyi, ga baki daya hankalin shi
a tashe yake itama kallon nashi take yi, meye ta tambaya tana kallonshi wai
Abbane yake tayani murya, wai a dazun nan Ummata ta kira ki a waya, kika gaya
mata mun dawo ne daga Asibiti likita ya tabbatar mana da cewwa kinda juna biyu
na tsawon wata biyu, dirshan ta fadi zaune barkewa tayi da wani matsanancin
kuka, shima, sulaiman zama yayi a dai-dai kusa da ita sai dai wannan karon ba
lallashinta yakeyi ba, hada tagumi yayi ta fada kogon tunani, shi ba abinya
fada ta gida ba, a can hankalin su ya tashi, kuma ma zai iya yuwa idan wani
yace zaizo a kasheshi a kan hanya sunfi minti goma anan zaune, sa’annan
Sulaiman ya mike ya iyadda bude kofar falon su duka suka shiga ciki, jawo
akwati takeyi itama suka nufi daki ji tayi kamar an ja mata kafa jicce ta fadi
kass ram! Yunkurawa tayi ta tashi amma ta kasa, wasu taurarin wahala ta ringa
gani sunayi mata yawo, yarda tashi akwatin yayi ya nufo inda take da gudu,
yanka kokarin tada ta, lumshe idanuwanta ta farayi, tun tana iya budsu har
takai ga duka suka rufe rungumeta yayi ya kwala uwar ihu, da hanzari ya
tallabeta da gudu ya fito baima tsaya ta wani rufe gida ba. Mijin Khadija yayi
kicibis dashi ya dawo, da karfi ya tsayadda mota, Sulaiman da gudu ya shiga,
Asibiti, asibiti! Da isarsu asibiti aka daurata saman keke da gudu aka wuce da
ita emergency, gaf aka rufe kofar emergency aka dakatar dashi daga yunkurin
shiga cikin dakin da yayi, jiginawa yayi a jikin bango emergency zaune yayi a
nan wurin ya fara kuka ne ya ringa lallashi da kyar da sidin goshin daina
hargowarda yake ya zama hawaye kawai ke zuba daga idanunsa, nurse c eta fito da
fara’arta da kafri suka mike su duka sister ya lafiyar jikinta, zan iya shiga
yanzu, don Allah ku bari na shiga nag anta, Sulaiman k eke jero wayannan zancen
duk shankalinshi a tashe relax malam cogratutaltion ma, wani kallo yake mata me
kikace? Cewa nayi congratulation matarka na dauke da JUNA BIYYU na tsawon wata
biyo, kuma zaka iya shiga ka ganta, za ma kaiya tafiya da ita, because she is
out of danger known. Bai jira ta kommala jawabinta ba yaruga da gudu zuwa cikin
inda dearest dinshi take, zaune ya taradda ita tana kallon yan yatsunta tsaye
ya tsaya cak, kamar tasan dashi ta daga kai suka hada ido, ya karaso inda take
ya rungumeta yana zubarda kwalla, Alhamdulillahi kin tsoratani, don sAllah kada
ki sake yimin irin haka. A nan aka sallame su daga asibiti maigidansu Khadija
ya maidasu gida, sukayi masa godiya sun ma rasa zaune kawai sukayi kamar masu
ansar gaisuwa, kiran mariba akayi, suka tashi sukayi alwala, ya jagoranceta
sukayi sallah, mikewa yayi ya fada kichen a dafa mata indomies, a wani bangare
na rayuwarshi harga Allah dadi yakeji mara misaltuwa, matarshi nada ciki, kenan
zai zama baba, zubo indomie yayi a flate ya kawo masu a nan bedroom dinsu
tareda rowan da zasu sha, aka kira isha’I suka mike suka sauke farali, suka
jawo kwanon abinci sukaci sukasha ruwa, ta tashi da dauki kwanuka da ni yar ta
kai kitchen karaf ya amshe, no wannan ba aikin ki bane yanzu, zauna ki huta,
kada ki wahaltamin da baby, duk da irin halin da suke ciki said a tayi yar
dariya, duk kunya ta lullubeta, ya dauki kwanuka yaje ya ajiye ya dawo, suka yi
addu’a suka kwanta. Wayyo!! Wata kara aka buga mai mai matukar firgitarwa
zunbur suka sauka daga kan gaso jan abu sukaji anayi a falo, kasan tys idan ana
jan abu akanshi zai ringa bada wani sauti daban, kuka sukeji anayi matsananci,
a hankali suka tattaka ya zuwa bakin kofar daki yaddazasu iya hango abinda ke
faruwa a falon, da baya sukaja da kafri saka makon ganin wanan tashin hankali
da basu taba gani shi ba, wata mace ce ko ince budurwa wace bata wuce shekara
goma sha takwas zuwa sha tara ba, ake ja, batareda suna ganin mai jan nata bag
a baki daya jikinta jinine faca-faca, kama kuwa kadan ya rage ya rabuda gangar
jikinta, rokonsu take tana kuka don Allah ku taimaka mini, karaja sukeyi da
baya suka rungume juna suka kankame waje daya, wuf tayi ta nufo su da niyar ta
cafke su, kamar an wulla ta ta fada can gefe daya, sake mikewa tayi kanta yana
shillo ta kara nufo su amma kamar a karon farko ma sake wurgata akayi, kuwa
take kala-kala iri-iri tana yunkurin kamasu amma ta kasa, su kuwa suka buga
suka kara ja da baya suncakankame juna, duk wani yunkuri, na shiga cikin dakin
tayi amma ta kasa Sulaiman ne yayi karfin hali ya ja kofar daki ya rufa da
karfi ya dawo daga baya. Duk hargowarda takeyi a kunnuwansu yake, addu’a suka
yi suka tottafa ko’ina suka haye kan gado ko runtsawa ba wanda yayi-sai yanzu
Bilkisu ta gano dalilin da yasa ta kasa shigawa acikin dakin, maganinda baban
nan ya btane, haka suka zauna ba wanda ya koda runtsa idanuwashi, sai a
shiyoyin asuba su duka bacci ya sace sub a tareda sun sani ba Sulaiman ya fara
falkawa, kasa rufe bakinsa yayi sakamakon kashin ganin matarshi da yayi akan
gado, kofa ya gani bude, a hankali ya tashi ya fara tafiya yana duba kofar, can
ya hango Bilkisushi a falo zauna murmushi, zo dearet, zo mu karanta Qur’ani
kama meye yayi kadan ya cuta mana, shi nake karantawa kazoo mu sauke Qur’ani a
yau dinna, ajiyar zuciya yayi ya sauke nunfashi da karfi okay bari na dauko
nawa Qur’anin, a’a ai gashi na dauko duka zo kawai mu karanta, fitowa yayi ya
nufa ci falon ya tsallaka ya fada cikin falon, sai dai kuwa abinda bai saniba
Bilkisunshi tana kwance sa bias gado tana sharer bacci abinta. Sai da gari ya
fara wayewa sannan ta farka itama kamar yadda Sulaiman yayi haka itama ta fara
duban mijinta har a toilet ta dubashi bata ganshi ba cak ta tsaya da taga kofa
a bude, a hankali ta fara tafiya ta nufaci kofar da zata kaita falo wani
faduwar gaba taji da bugun zuciya tsallako kofar tayi ta nufo mijina kam ta
kame tsaye akan matsanancin tashin hankalin da taji, mijinta dearest dinta ta
gani a zaune da wasu kananan kayan da hula da wasu rufaffun takalma kai! Sak
shigar USMAN! Yadda yake zama, yadda yake kada kafa daya juye hularda yake yi
kai! Kome sak na MAN! Daga kai yayi ya fara dubanta tun daga sama har kasa,
itama suban nashi takeyi, nikewa yayi kau!! Ya wanka mata wani hatsa bibin mari
said a ta fadi ta fasa bakin ta, kamar wanda ya dawo daga hayyacinsa y ace
cikin wata murya wadda ko ba’a gaya maka ba kasan mace c eke wannan murya,
yanzu idan Usman yaji yanda nayi miki fa ya fara dube-dube kamar wanda yaga
usman din a falon, da karfi kuma ya juyo ya kalleta kallo irin na mugunta da
tsananin kiyayya yaci gaba da Magana wannan dai ta mata, idan na kasha ki ai
bai zai taba sani ba yana fadi yana cize hakoranshi, ya nufaci inda take ya sa
hannun ya cafko wuyanta ya dagata dashi sama har ya cirata har karfi aka banko
kofar shigowa falon! Tsohon nan ne da suka saba dashi, da karfi ya wankada
mashin wasu ruwa da suke rike da hannunshi, wai gowa Sulaiman din yayi da karfi
suka hada ido da tsohon, wurgarda Bilkisu yayi da karfi ya sheka ya nufi bangon
falo tuma yayi ya tsunduma cikin bandon baya bace. Baban yaje ya tayadda ita
kuka takeyi kamar ranta zai fita, ba dai Usman ne keyin duk wannan abinda ke
faruwa ba, take fadi tana kuka mai tsanani. Ba Usman bane ke muku wanna abun
amma sanadiyar sa ne duk wannan abun ke faruwa, how? Tayaya? Ina mijina kuma
wane sanadine na Usman aka da yake faruwa dan haka ta fada tareda zubewa a kasa
tana kuka. Gyara zama yayi ya fara fadi mata kamar haka --------
Ku biyoni a littafi na biyu dan jin
cigaban kayatacce labari.
Taku mai debe muku kewa Asiya Sadiq Maccido
(Asikhan)
No comments:
Post a Comment