HUBBUL YAKIN cigaba 3
ASIYA SADIQ MACCIDO
(ASIKHAN)
Copyright © Asiya Sadiq September, 2017
Hakkin Mallaka (M) Asiya Sadiq September, 2017
Published in Nigeria by
Sharhamak Computer Ventures
Beside Birnin Kebbi Local Government Secretariat
Kebbi State, Nigeria
Tel: 08113777717
Book 1 of HubbUl Yaqeeen Series 3 |
Suna zaman su lafiya da Sulaiman abin sai ace san
barka. Misalin karfe sha daya na dare yaji ana tadashi daga barci buda ido
yayi, me zai gani farin cikin rayuwarsa ce Bilkisu a tsaye taci ado da wadansu
kananan kaya masu jan hankali, tasha kwalliya ta fitar hankali sai kamshi
takeyi mai matsanancin dadi tsaye take tanayi masa wani mayen kallo ai kuwa bai
san sa’ada ya tashi zumbur ya mike ba, ta dan ja baya kadan ta bude hannuwanta
biyu alamar yazo, saikuwa yayi kai tsaye inda take amma sai ta goce tana mai yi
masa dariya. Au ni zaki wasawa haka da gudu ya bita suka fada sai a falo da
gadunshi a tsaye yayi chak----- sakamakon ganin Bilkisun shi zaune a falo tana
kallon Series dinda take kallo ko yaushe mai makon tufafin da ya biyota dasu
kuwa rigar baccin da yasan Balkisu da ita itace sanye a a jikinta da saurinta
ta mike da sauri lafiya dearest me ya faru naga ka shigo haka da gudu lafiya.
Bai samu ta cewa komai ba mamakin ya hanashi Magana ga baki daya sai a ranshi
yake Magana ba yanzu na biyo Bilkisu da gudu ba, idan dai ga Bilkisu nan a
zaune to waccan wacece na biyo kafin ya samu amsar wadannan tambayoyi na Bilkisu,
ta sake tambayarsa lafiya baka ce komai ba, menene? Murmushin yake yayi yace
babu komai amma da yaga Bilkisu na tantamar abinda ya fada sai yace mafarki
yayi wai tana nakuda akace ya sheka ya kira likita shine ya shigo wai, dauka ta
gaskiya ne. fashewa tayi da dariya tare da ajiyar zuciya dauke indonta tayi
akan nashi yanzu dan wannan gudunne zakayi in akace ka kira likita? Dariya
kawai yayi batare da ya bata amsa ba, zuwa yayi ya kashe kayan kallon, chak ya
dauketa, dama dariyar takeyi harda ma shakewa, Malama (is time for bed now),
sai daki ya ajiyeta ya maida kofa ya rufe. Gobe (workers day) kamar kullum
ma’aikata suna hutu, Sulaiman tunda safe yasa
Bilkisun shi tayi musu girki mai dan yawa yaje ya dauko motar ofishinsu ya
dauke ta sai babban (park) din kaduna sun yi nishadi sosai. A can basu wani
dade da zuwa ba, yace bari ya daukota su zaga gari domin taga Kaduna tunda yau (free)
yake a cewarsa yau wata babbar damace daya samu, anan take kuwa Bilkisu ta
amince da wannan shwarar, sun zazzagaya wurare da dama balkisu ta bude ido, a
gaskiya Kaduna babban birni ne mai kyan gaske. Bari muje bakin ruwa ko Balkisu?
Da hanzari ta amsa masa da eh muje, dama kamar yasan abinda yake rantane ba
abinda Balkisu keso daya wuce wurin ruwa. Tafiya suke kowane ranshi cike da
farin ciki, ‘yar fira suke gwanin ban sha’awa. “Wai ni ko in tambaye ka mana”
Balkisu ta fada tare da kallon Sulaiman, eh ina saurarenki yace batare da ya
kalleta ba kasancewa driving dinda yakeyi, halama dai baka son zama cikin
mutane ne? Me yasa kike fadi haka? Sulaiman tare da yi mata wani kallo mai
dauka da alamar tambaya kawai dai naga daka tashi nema mana gida ne sai ka nemi
layin daba mutane a cikin sa mutane saura duk irin gidajen nan ne na manyan yan
siyasa da suka yi domin kawai idan sun shaqi iska suzo suyi dan hutun sati biyu
su koma ni ma tunda nazo duka gidajen da ke side dinmu masu gidan ko sau daya
basu taba zuwa ba, sai kuma sau daya gidan da muke (facing) suka zo suma basufi
(two weeks) ba suka wuce, su kuma gidajen nan hudu da suke akwai mutane aciki
uku duk (cristian) ne fah. dayan kawai ne musulmai su Khadija da Fatima kuma
suma bawai kusa da gidanmu suke ba. Hakane amma ba yanda kike nufi bane, me zai/sa
na ki son zama acikin mutane bayan cikin mutane na tashi, Allah dai ya nufa nan
zamu zauna shi yasa, kuma banda abinki ba gani ba koda bamuda maqota ai kullum ina
tare dake kamar inuwa ya fada tare da murmushi itama murmushin tayi, hakane (Dear)
af dazu ko na manta na gayama Umma ta kira tace na gaisheka, ina amsawa ko
mutanen gidan ina fatar kowa lafiya, lafiya
qalau, madallah,, Bilkisu mun iso, a dai-dai lokacin da suka iso wurin ruwa
yayi parking ya fito ya budewa Bilkisu itama ta fito tare da fadin (thank u)
bude boot din mota yayi yafito musu da babban (carpet), ita kuwa Bilkisu ta
bude sit din baya ta dauko abinci wuri suka nema mai ni’ima suka shinfida suka
zauna, bilkisu ta dibar masu abinci suka ci, kasan garin Kaduna baban birni ne
dab a wanda ya kula da wani, bayan sun kamala cin abinci suka dan taba hira
irinta miji da mata suna tsakiyar firar ce Sulaiman ya hangi mai sayadda Tuffa
wato (Apple), Bilkisu bari naje na siyo mana apple yanzu na dawo, ya tashi ya
nufi wurin wai sayadda Apple, kai mai Apple nawa Apple, din, ya sayi apple din
ya miqa masa kudi ya jira shi ya bashi canji, juyowar da zaiyi ya dubi gurinda
Bilkisu take, me zai gani ya gani wata mata sani dai-dai sa’ar Bilkisu ta rige
Balkisu a tsakiyar ruwa tana nutsar da kanta da gudu ya rugu ya watsar da (Apples)
dinda ya siyo Bilkisu!Bilkisu! gudun yake yana kiran sunanta, ita kuwa wannan
matar a dai-dai lokacin ta nutsar da ita gamin da tsoma kanta cikin ruwa
Bilkisu nata kokari amma a wanna karon sai ganin yayi kafafuwanta dake motsi
sun daina, har yanzu matsanancin dugu yakeyi yana kiran sunan Bilkisu, bai Ankara
ba sai ji yayi tuntube sai kasa ya fadi ya wuntsila duk da haka mikewa yayi da
sauri ya sake ruga wa. Ga baki daya mutanene da ke wurin kallan sa suke yi, ji
yayi, kamar daga sama murayan Balkisu a bayan shi, bai fasa gudunda yake yi ba,
ya dan juyo kadan, me zai gani Balkisu ce kuwa take binsa da gudu tana kiran
sunan sa tsaye yayi duba cikin ruwa yayi a inda yaga wata tana kokarin kashe
masa Balkisu shi, ba kowa wurin lokacinda ya juyo inda Balkisu ke gudu tana
kiranshi, har balkisu ma ta karaso idonta cike da kwallah ganin irin mummunan
faduwar da yayi, da zuwa rungume shi tayi ta fashe da kuka lafiya Dearest mike
faruwa gani ana, ina inda ka barni banje ko inaba meke faruwa? da kyar ya hada
yawu da suka lake masa, numfashi yake sama-sama Alhamdulillahi Balkisu tunda
kina lafiya ba abinda ya sameki, dauko kaya mu wuce yanzu-yanzun nan kasa
Magana yayi, ga baki daya mai Apple ne ya iso bakin mota, Alhaji ga canjin ka
fa da Apple din da ka saya, said a Sulaiman ya dan tsaya kamar mai nazari sanna
ya ansa, ya wuce ya bude mota ya tada suka wuce gida, ba wanda yake Magana a
cikinsu. Ita Bilkisu tunanin ta keyin ya akayi mutum ya barta zaune sanna ya
dawo a guje yana kiran sunanta har da wannan irin faduwa haka? wadda tayi
sanadiyar daya fasa. Hancin sada jinni mike damin Dearest dinta me ya gani ne
haka lallai koma meye ba lafiya ba, amma ba yanzu ya dace tayi masa Magana ba
kamata yayi ta bari sai sun iso gida hankalinshi ya kwanta sannan, domin yanzu
yana cikin rudu da fargaba. Shi kuwa a bangaren Sulaimn ga baki daya kansa ya
kwance stabbas yaga wata tana yunkurin kasha balkisu yasan lallai yaga haka to
amma kuma ya akayi bayan da ya sake dubawa yaga ba hakanan bane, idan dai
balkisu na can a inda ya barta da yaje sayen Apple to waccan da ya gani wace? Wacce
wadda kuma ta yi yunkurin kashe waccan Balkisu? anser day a kasa ganewa kenan
har ya iso gida bayan ya shiga ya bude gate ya shiga da mota ya kulle gate ya
dawo, ya taradda Bilkisu na jiranshi a kofa suka shiga taje, kai tsaye ta dauko
first aid box ta bashi taimakon gaggawa, taje ta mayar da magungunan ta kuma
biyo mashi da ruwan sanyi, ya ansa yasha, bayan kamar minti biyar ba wanda yace
uffan sai Bilkisu ta katse shirun da tambayar shi ko lafiya game da abinda ya
faru dazu? Ya so ya gaya mata sai kuma ya tuno da cewa Balkisu mace ce idan ya
fada mata zai kara dagula lissafi ne kawai. Domin haka yace ta barshi ba komai
bane amma sam taki amincewa da haka, da dai yaga tanace akan sai ya fada mata
sai ya maida abin ba’a yace yana ganin sonta ne yake neman zautar dashi, duk da
ta san ba haka bane ama sai murmushi ta sharer da maganar kamar yadda. Taga
baya son zancen, tun daga wannan lokacin bata sake tamabayarshi ba kuma, yayi
kamar sati baya wani sakewa sosai ko office yaje zai yita kiranta yaji ko
lafiya, amma sannu a hankali anaka manata da wannan abu komai ya dawo normal a
kaci gaba da yadda aka saba, yau asabar su Balkisu sukayi baki abokanshi Nuhu
dashi da matarshi a gidansu, suke wuni sai bayan magariba suka wuce tare da alkwarin
suma wani sa’I zasu je suyi masu yini kamar suma yadda suke yi masu. Bayan wuce
war su Nuhu Sulaiman yasa Balkisu tad an dafa masa abinda zasu ci domin ba
sauran abinci a gidan kasancewar bakin da sukayi sunada zara, kitchen ta shiga ta
daura abinci macaroni ce yar two minute ta aza musu, ta dauko timatir fresh
tana yankawa harma ta kusa kareyankawar, daya kawai yayi saura maid an girma
haka, yanka wanda zatayi sai kawai taga jinni ya fito cikin tumatirin, sake
dubawa tayi kamar dai wadda ta tashi daga mafarki. Tabbas haka dinne jinni ke
zuba daga jikin tumatirinda ta yanka, baya-baya ta farayi tana duba ttimatirin
me zata gani saurantimatirin data yanaka ga baki daya wasu irin tsutsoci ne ke
fitowa daga garesu ta ko ina kara yi tayi da baya tana shirin guduwa sai kawai
tayi kicibis da Sulaiman, lafiya? A firgice sai juyawa tayi tana nuna timatir
din. Me ya faru yankewa kikayi wajen yanke timatirin ko shiru tayi ta kasa cewa
kome a, sakakamakon ganin timatirin da tayi lafiya kalau ba abinda ya same shi,
ba wani jinni bare kuma wasu tsutsoci dake sukuwar sallah a sama a.a da rasa ta
fada tayi to meyee haka? mike faruwa ne day a dauki tumatitrin abinda take fada
bay a dauki tumatirin da kanshi yasa cikin tukunya ya juya kinga jeki zauna yau
zakici girki mai dadin da baki saba cin irinshi ba, kasa tafiya tayi saida yazo
ya fitar da ita da kanshi Sulaiman ne yayi masu sanwa sam bata iya cin abincin
da kyarya matsa mata ta danci kadan, abincin ba, ku fa mata haka kuke idan
kamala shirin ba, ku fa mata haka kuke idan dai mutum yace ya jira ku to shi
kuwa sai ya shiga uku da jira Sulaiman ya yakema Bilkisu bita, na kare ranak ya
dake muje ta fada tana dariya tare suka fita suka kulle gida ya dauketa wurin
saloon suka, nufa can kan titin shigowa layin su. Sai a bakin shagon ya ajeta
tare da bata kudin saloon din har ma da Karin, idan aka kare sai ki kirani
sinzo na mai dake gida murmushi tayi tareda fadin nan wurin ne har sai ka dawo
daga office dinku ka mayarda ni sanna ka koma? Malam ko cikin dare ne ai zan
iya mayadda kaina ballantana zanzu da rana kiri-kiri. Shima murmushi yayi yace
to kinga laifina ne ina tsoron kada ki bata ne kinsan Kaduna da fadi idan kika
bata a in azan nemoki, har ganoni ne wani abin wahala ni ai ko a brining sin ka
bat azan nemoka, ke kin kuwa san ko inane birnin sin kinsan yawan mutanen da ke
cikinta, Dearest bari ta yawan mutane ko a Birnin ALJANU DA FATALWA ka bata
wallahi ni Blkisu sai na nemoka koda kuwa zan rasa rayuwata ne. wani irin dadi
Sulaiman yaji musamman da yayji irin tsantsar kaunar da Balkisun shi take
mishi, allah ko matata? Ya tambaya yana main zolayanta ko shakka babu ta fada
tare da taba kundar ta suduka suka fashe da dariya, to bari na wuce office kar
naje na dade na bata nasa matata cikin wahalar nemana, sake fashewa sukayi da
dariya ya tada mashin dinshi bye love ya fada tare da kashe mata ido daya
murmushi tayi see you soon ta sfada ta kuma hanyar shiga cikin shagon saloon
din, sai da ta shiga cikin shagon sanna ta juyo shima Sulaiman a dai-dai
lokacin ya juyo suka hada ido dariya yayi ya daga mata hannu alaman bye bye
sanna ya juya yaci gaba da tukin mashin dinda yake yi, murmushi kawai tayi ta
karasa shiga cikin shagon excuse wata mata ta amsa da yes shigo. Sannu fa ga
wuri ki zauna ta zauna, ta zauna tareda fadin nagde me kikeso ne madam inji mai
shagon saloon sdin nazo sa mai ne okey bada bata lokaci ba ta fara cikinta
shigar Bilkisu drayer kada wuya sai ga wata syarinya yar kimanin shekara sa
takwas ta shigo a cikin shagon da gani basai ka tambaya ba kasan ‘yar mai shgon
ce domin tsananin kamarsu day abaci said a ta gaida Balkisu sannan ta koma kan
maaifiyarta dauke take da kwan abinci da kuma wani jug da drinks aciki, mummy
ga abincin na qare ni zan koma shagon, wani dan karamin siket ne iya gwaiwa
tasa duk ilahirin jikinta a fili kai gaskiya ya musulunci nada dadi shine addinin
dake mutunta ‘ya mace ya kare darajar ta da martabarta. Ita dai madam abincin
wanda ke nuni da da cewa dama a jiraye, take malama muna kwarya fa please kici
abinci a’a nagode wallahi, kici kawai ni a koshenake kallon abincin tayi, ta
kasa gano ainihin menene kamar soyayyar doya amma kuma abin ya banbanta to meye
haka gwanin ban sha’awa, taso tayi shuru sai kuma ta tuna matambayi baya bata
kuma ma ai karuwanta ne, madam menene haka kamar soyeyyar doya domin saloon shi
zanyiba, irin na soyayyar doyar doya bace. Haka ne wannan ba doya ta mikawa
Balkisu kici kiji yanda yake yafi doya soyyaya dadi sossai da kyar balkisu taci
aiko gaskiyarta gaskiya abinnan nada dadi sosai ya akeyin shi ne Madam. Bata
jira ta kammala cin abincinta ba ta fara gayamata farko zaki dan dafa doyanki
amma kada ya dafu sosai, kamar irin far-builing dinta tattasai da albasa, sai
kuma ki fasa kwanki kisa spices dinki ki gurje, doya da kika sauke kuwa sai ki
gujeta kaman yanda kike gurje yakuwa, ba wai yayi gari ba kinsan bata wani dafu
ba, bayan kin gama gogewa sai ki zuba tarugunki da tattasai da kika daka tun
farko ki gauraya ko’ina yaji, ji dan kara species dinki bada yawa ba sai ki
kawo kwanki ki zuba ciki, shine ki gauyraya, sai ki samu leda kisa kamar dai
yadda akeyi alala ki kulle ba sosai ba sai ki saka a ruwa zafi kamar zakiyi
alala idan yayi da kin duba zaki gane, sai ki fitar kiyi masa shape din da kike
so. Great gaskiya nagode, fah madam na karu sosai thank you onces a gain
Bilkisu ce ta fada, madam kuwa sai faman budar baki takeyi itafa nan ganin yake
ta burge. Sosai, no ai wannan is notting, shiru tayi kamar wadda ta tuna wani
abu sai kawai ta tsayyoma drinks dinda yake cikin jug Balkisu ta kawowa malama
ga wannan kisha ‘yar gajeruwar dariya balkisu tasa a’a gaskiya ki barshi kawai
nagode ko wancan dana ci domin nasan ya dafuwanshi yake idan na dafa ne ki
barshi nagode Allah. Malama Balkisu meyasa nace kisha ba ko wannan drinks din
hadashi akayi kuma yanada dadi, sosai nasan mai gidanki zai so shi sossai shiru
Balkisu tayi cikin ranta tana dariyar madam domin tasan wannan ba komai bane
face dadin yabon da tayi Balkisu tayi mata, zugata da taji anyi duk shi ya janyo takeso ta kara
nunawa Balkisu ita ce kwaruwa ce wujen iya girke-girke. Karba kofi kawai tayi
ba tareda tasha ba drinks din menene na cocumber ne da kwakwa a lokacin ta dan
ka baki ta kurba kai? Gaskiya shima ya hadu. Cocumber da kwakwa shi kuwa ya ya
akeyin shi, ai madam bata jira ta kammala maganar da takeyiba ta soma; farko ki
fere cocumber ki sai ki yayyanka ki saka a bander ki blende ta sai ta blendu.
Sosai sai ki kawo kwakwa itama ki blader
ta cikin cocumber idan kuma kin gama kina iya blande su tare, sai ki saka
madara a ciki kisa cikin frige shikenan kin hada drinks dinki, kuma wani abin
burgewa das hi drink dinnan bawai kawai dadin shi kesa ayi shi ba a’a yanada
matukar amfani a jiki sossai. Gaskiya madam nagode sosai naji dadin zuwa saloon
wurinki domin na karu da abubauwa sosai, kinga yanzu ko kina karemun gyara kai
na zanje nayi abubuwannan da kika koyamin sauri karemin naje so drink suka
fashe da dariya, madam ko ta gyara mata Kanata fes-fes gwanin ban sha’awar har
bakin shago ta rakayota sukayi bankwana Balkisu ta wuce. Bata zame a ko’ina ba
sai gidan su khadija da Fatima yan layinsu can ta nufa tayi kwatanta mata inda
ake sayerda kwa-kwa domin duk abinda zatayi aiki dashi tanada kwa-kwace kawai
batada, tayi kokarin kiran Sulaiman a waya Switchup tana sane ta gayamai zataje
wani wuri ba zata dade da text, Sulaiman
dinne yake gayamata zai kai dare kada ta jirashi akwai meeting dinda
zasuji ne kuma ba dole zai kasha wayanshi sauke nunfashi kawai tayi kutsa kai
gidan su Khadija da Sallamarta Fatima kadai ta cimma Khadija batanan ta fita
anguwa, tayi sa’a yar cikinsu Habiba nanan kuwa, ita ta aika ta siyomata,, ita
kuma ta koma gida, kai tsaye ta nufi daki ta saukar da akwatuna gaba daya ta
bude ta kasan sai data fitarda rabin kayan sanna ta kai ga wasu tulin kanan
kaya ma’aita English wears, said a tad an tsya zabe sanna ta ciro wasu jajayen
sun hadu matuka murmushi ta saki, lallai aminiyarta gwaruwace duk ita ta saya
mata kananan kayan nan dama a inda ta dialiara kenan Asikhan? Asikhan ta fada
tana dariya ta tuna irin mitarda tayi mata game da kayannan data saya mata, da
gaskiyar aminiyartata duk cikin kayan ba Wanda bai kai matuka ba wurin kyau,
kai wai ita Asikhan tana da kayanda tabawa muhimmanci ne da suka wuce kananan
kaya? Dariya kawai tayi ta ajiye wadanda ta ciro Akan gado ta shiga mayadda
sauran kaya ta maida akwatuna yadda suke, sannan ta fara gyaran gida ta shiga
aiki tukuru baji ba gani tad an canga wasu kuwa duka ta maidasu falo ta
bubbuga, komi yayi gwani ban sha’a. daganan kuma ta fada kitchien ta fara
ferewn doya kenan taji bugun kofa da sauri ta nufaci kofa koda ta bude Habiba
ta gani da abinda ta aiketa ansawa tayi, ta kuma yi mata godiya Habiba ta miko
mata sauran canji naira talatin ne suka rage ki barshi kawai ki dauka na bakai
in kinje kice ina gadasu kinji nagode Habiba tace tareda washe baki zasuji
nagode Amarya ta sake fada, murmushi kawai balkisu tayi ta rufe kofa ta koma
bakin aiki bata manta ba yadda madam ta gayamata haka tayi, kamar ko ba ranar
ta farayi ba domin tayi dai-dai yadda akeso koma tayi kyau sosai ta fidda shape
dinda takeso ta rufe a kula ta kai dany ta hada drinks dinta a hakikanin
gaskiya yau ta aikatu, ta kamala hada drinks dinne a kayi kiran magariba, ta
saka shi afrige ta shiga bandaki ta doro alwala ayi sallah, bayan ta idar da
sallah ta koma kitchen ta wanke kwanukan da tayi aiki dasu ta goge kitchen din,
sannan ta nufi frige ta dauko kankara ta faffasa ta saka ta sake mayadda drinks
din a cikin frige, kiran salla isha’I taji taje tayi sallah, ta cire kayanta ta
nufi bathroom har takai kofar shiga toilet din kuma sai wani abu ya fado mata a
rai, falo ta nufa ta bude kofar falon tad an iza kofar ta yadda idan mutum ya
iso daya dan tura kofar zata bude sannan ta nufi daki ta rufe kofar dakin amma
a wannan karon dakin kalloshi tayi ta yanda idan dai ba ita da take ciki ba ba
wanda zai iya budewa, dariya ta saka sanna ta fada toilet tayi wanka abinta
bayan ta kamala wankan a gaba dressing mirrow ta tsaya, tunanin irin kwalliyar
da takeyi sanna ta zauna ta fara zuba kwalliya bata kammala kwaliyarada takeyi ba
can a falo taji sllama dearest dinta, salamu alaikum Honey in Home ya kara fada
dariya kawai tayi, tace gaba da kwalliyarda takeyi, kai waye daki ya nufa wai
ina masu gidanne, za kofar dakin yayi ya kuwa jita gam a kulle, a,a Balkisu
lafiya dariya ta sake sakawa malam kaje falo ka zauna zan fito nan da minti
biyu shiru yayi duk mamaki ya cika shi as you wish my lady na fada ya komo falo
ya zauna, sai kamshi kawai ya keji yana tashi, dama ko yunwa yakeji, ita kuwa
Bilkisu saka kayanta takeyi ta bude yar karamar kit ta dauko agogo ja ta saka
ta sake komawa a gaban dressing mirow ta kalli kanta masha Allah ita karan
Kanata tasan ba karamin kyau tayi ba, hakika aminiyar tat a cancanci yabo
wayanna kayan haka, wana murmushi ta sake, ta jayo turaruka kala-kala a fara
yiwa kanta wanka dasu bancin na jikinda ta shafa kafin ta saka kayan kanshi
ba’a cewa komai, kofa ta nufa ta bude a hankali sannanta leka wata yagogan mata
ya kasa hakuri harya isa diny ya fara bude kula fitowa tayi ta tsaya ajikin
kofar nade kafafuwanta tayi ta aza daya bisa daya sannan ta jigina a kan kofar
hannunta kuwa dagashi tayi sama ta mannashi da bango, irin tsayinnan dai tayi
nay aka gannine, irin wanda karishna kapoor tayi a cikin film din raja
Hindustani wani kamshi ta doki hancin Sulaiman a yayinda yake kokarin bude
kular da ganin fuskarshi yayi ya dubi inda kamshi ke fitowa, la haula wala
kuwati illa billah!!! Mikewa yayi ai ya saki baki wacece wannan yake gani haka
Bilkisu ce kallonta kawai ya keyi bakinshi a bude da murufin kula a hannu tazo
tayi dariya amma kuma sai ta kanne wata irin tafiya takeyi kamar batason taka
kasa karayraya jikinta takeyi ta yanda ko ina nata motsi yakeyi, frige ta nufa
ta wani dan duka ta zaro jug dinda ta saka drinks a ciki, a saman frige din ta
jayo kofunan jug din guda biyu ta nufo dany din. Har yanzu tsaye yake yana
kallonta kamar wata baindiya yake ganinaka shi ga baki daya yama rasa me yake
ciki, yama manta da yunwarda yakeji shin wai Bilkisu ce haka, ajiye jug wani
zaburar das hi. Cikin kissa da kisisina irinta wayayyin mata, sannan ta anshi
murufin kular ta ajiye ta ciro flet ta zuba masu abinci ta ciro fork daya ta
ajiye a gabanshi, gab aki daya rasa ta cewa yayi, to muna zaice daukar fook din
yayi a sannan ne ya tuna da yunwarda yakeji ya fara cin abincin yana kai loma
ta farko a baki lakuwati! Wani irin dadi yaji ya kamashi. Har kunne, ya kara
dibo ta biyu ya ci sai a sannane ya lura Bilkisu bata ci, lafiya baka cin
abincin ne ya tambaya yana kallonta bata fuska tayi kamar zatayi kuka dazu ne
da ina fere doya na yanke hannuna Magana takeyi cikin salo irin na shagwaba,
ajiye spoon din yayi mu gani sannu --- injin bakiji ciwoba sosai, bari na dauko
first aid box da kyar ta kanne dariyar da tayi kokarin fito mata yanda taga
yanayi abin gwanin ban dariya dan taliki dukya rude, a’a ka basrshi kawai ya
daina yimin zafi sosai, to bari na baki abinci ko da sauri ya fada yana
dubanta, dama haka takeso nufinta kenan, daga kai tayi cikin shagwaba tace to,
ci yakeyi yana har said a su duka suka koshi, sanna ta tashi ta zagayo ta zuba
drinks din a kofi ta tattako dai-dai inda yake said a ta wani kwanta mishi
sanna ta fara bashi a baki, rasa duniyar da yake yayi da mai zaiji dadin drinks
din ko kuwa Balkisu da take kokarin zautarda shi, nan take ya shanye, ta
tambayeshi cikin wani irin kasha murya a karo tana wani murmushi mayen kallo
daga kai kawai yayi batareda ya samu Kalmar eh ta fito ba, ta kara tsiya
yamishi ta bashi a baki nanma ya shaye a karamaka ta sake tambaya sake daga kai
yayi kamar wani dan karamin yaro wanda bai iya Magana ba, duk iya kannewanda
tayi wannan karon said a tayi dariya ta yanda ba zai gane dashi take ba duk da
tasan ya koshi baya dai iya cewa ya koshi ne said a ta fara tsiyayowa kafinta
kai masa a baki, sai ji tayi ayi wani irin gyashi da kyar ta iya hadiye dariya
tace anya Dearest baka kishi ba, na’am eh nakoshi gaskiya kam, saura ke mana
kasha, daga kai tayi tareda fadin uhum ta tashi ta nufi kujerar ta a fara shan
drinks din, kallonta yakeyi kamar bai taba, ganinta ba ita kuwa tana sha tana kallonshi
yanda taga yanayi kamar zai hadiye ta saura kiris tag ware, tagama sai tace
masa miasa na koshi, dan gajeren murmushi yayi tau, bata jira yace wani abuba
ta fara daukan kaya tana kai kitchen, dama ai kin barsu sai gobe naga dare yayi
kome kike gani, dare fah kace yanzu ko karfe tara tayi ne duba agogonshi yayi
au da gaskiyarki fa tara da minti takwas ni ca nike dare yayi sosai goben na
kai sauran wayanda bankai ba, shima murmushin yayi ba tareda yace komai ba, zo
muje yau za’ayi wani film dinda nakeso sosai farin wata ta wuce kawai batareda
ta jirashiba, da sauri ya taso ya biyota wane fil ne? Marokon zamani kasan ko
sau nawa zan kalleshi bana gajiya taje ta kuma kayan kallo koda suka kawo harma
an fara ta nemi go ta zauna shima ya zo kusa ta ita ya zauna, ta lura dashi,
kamar yana so yayi wata Magana kawai yi tayi kamar bata ganeba, sai can yayi
dan guntun tsaki, kinga nama manta banyi wanka ba, ni da nace ina zuwa ko
abinci baznci ba zanyi Wanaka, dauko idanuwan ta tayi akan kallon da takeyi hakane
fa kaga nima sam na manta, mikewa yayi yanufi dakii harda dan tuntubeshi, ya
fada tailet yayi wanka sanna yasa wata doguwar riga baka ya dawo falo ya zauna
wai yanzu naji wani irin iska yana shigowa juyowa tayi ay hark agama wankan,
ita dai tasan baifi minti hudu da yabar falon ba wannan wane irin wankane haka
ta danyi murmushi, eh harna kare mana ko kinga nayi sauri ne? a’a tambaya kawai
nayi, wurin wani dariya akayi musa mai sana’a ne kun sanshi wajen iya acting
dariya ta saka harda shakewa kallonta kawai yakeyi shi kwata-kwata baiga abin
dariya acikinba sai a lokacin ya kula a yanda aka canza wasu abubuwa da yanda
ta mayadda sauran lamination dinsu a falo, akice yau an canza tsarin gida oh!
Wai sai yanzu kai ka gani dama ta fada tana dan noke kai gaskiya yayi kyau,
murmushi kawai tayi, Bilkisu yau kinsha aiki, kika gyara gida haka sanna kuma
kika dafa abinci da idan mutum yaci baya iya Magana akan dadi gaskiya im the
luky husband in the whole universal kuma wai kinga yanda kikayi kyau kamar irin
‘yar tsawar nan Barbier kinyi kyau fiye da yanda kike tsmmani fah. Wani tashi
tayi yanda tayi yana kodata haka, tashi yayi ya nufi inda take kashin kanta ya
taba sannan kuma haka sai kace na indiyawannan dariya ta saka don Allah malam
dadin bakin ya isa haka, Allah ba dadin baki nakeyi ba ni dai yau nama rasa me
zanlawa tantaki dashi wurin haduwa murmushin dadi tayi tace “hauni” Balkisu
kinsha aiki da yawa ya kamata ace kinje kin kwanta dariya ta yi tace waya
gayama ba yaje ya kasha kayan kallo yace muje ka? Mikewa tayi tsaye amma sai
duk ta wani langwabawa kamar zata fadi yadai yafada, kafafuwana ne sukeyimi
nauyi cikin shagwaba, ai cak ya dauketa ya shiga daki. Balkisu ke faman gudu
wani katon mutum yana binta kuwwa take ta faman bugawa amma ba kowa a wajen a
jikin wani bango ta fada, shi kuwa katonan ya tsaya a gabanta ya rutseta kuwwa
kawai take famanyi, hannu daya yasa ya shaketa a hannu dayan shi kuwawata irin
wukace doguwa daga wukar yayi sama dana kokarin soka mata wukar yayi sama
girgiza kai takeyi tana fadin a’a duk idanuwanta sun firfito alamun firgita,
amma koa jikin katon nan, da karfi ya nasa mata wukar ta kwala uwar kara mai
tsnanin karfi. Maigado!!! Da karfi ummah ta farka tana kururuwar kiran sunan
diyarta firgigi shima malam iro ya fara a sakamakon hargowar da yaji matarshi
tayi. Lafiya? Meke damuwanki? Me akayi? A firgice tace mai gado? Maigado! Wani
ne da wuka -------- ta kasa idarda zancen duk ta firgita da ummunan mafarkinda
tayi dakata ba sai kin fadi abinda kikayi mafarki ba sherin shedan ne kawai shi
yakeso yayi wasa da tunaninki, tukunna ma dai kinyi addu’a ne kafin ki kwanta
sai da tayi shiru na dan lokaci har a lokacin a firgice take sannan ta tuna da
batayi addu’a ba a sakamakon dan kishin gidawa kawai tayi bacci ya shareta a’a
banyi ba ta amsa masa kingani ko shedan ne kawai shi yasa addu’a takeda
muhimmanci a rayuwar musulmi tayama za’ayi mususlmi ya kwanta baiyi addu’a ba
wadda idan kayita ba aljani ba har mutum bai isa ya cutar maka ba, wallahi dan
kishingidawa nayi bansan sa’adda ma bacci ya kwasheni ba malam, amma ina ganin
kamar Bilkisu tana cikin wani mummunan haline ko kuma wani mummunan abu yana
shirin faruwa da ita ni naji ----- don Allah kibar wayannan shirmen baxaki nemi
wuri ki kwanta kawai daga kinyi mafarki, to ance miki mafarki gaskiyane, shifa
mafarki kasha biyu ne, na alhairi daga Allah ne na sharri kuwa daga shedan
Bilkisu na can lafiya kalau da mijinta ba ke kika gayamin da rana cewa ta
kiraki kunri wata hart ace tana gaidani, ba? Daga kai kawai tayi alamar ah kiyi
addu’a kawai ki kwanta Bilkisu na lafiya kalau ba kuma ba abinda zai same ta
sai alkhari da iznin Allah. To malam, harta fara addu’a sai kuma ta juyo ta
dubashi tace malam kanada kudi a waya na kirata naji hankalina zaifi kwanciya?
Kira! Zanzu kinsan ko karfe nawa ki kira ta yanzu cikin wanna tsohon daren abin
ma ai gwanin ba dariya, yarinya da mijin ta haka kawai ki kirasu yanzu ki tada
masu da hankali ko, ba halin ta kara cewa wani abu domin ta lura maigidan nata
ya fara hasala dole tayi addu’a ta kwanta ba domin tana jin wani bacci ba sai
domin hakan ya zama dole gareta ne, sam bacci kasa daukar ta yayi ita kawai
tasan abinda ta gani Allah dai ya nuna mata goobe da safe lafiya dole ta kira
taji ya ake ciki. A bangaren malam iro kuwa tabbas yasan maid akin sa taji
tsoro sosai dangane da mafarkinda tayi amma ba yadda zai yi dole wannan hanyar
dayabi ita kadai zai yi domin ya tasa abin a zuciyanta karshe yazo ya dameta,
Hmm koma da menene Allah ya fefaddashi ya juyoshi zuwa alkhairi amen haka dai
yayi ta sake-sake ba tareda ya dade ba bacci yayi awon gaba dashi. Tunda
sassafe ummata aika aka siyo mata kati ta bayar aka saka mata a waya number
Bilkisu ta danna ta kira. Ita kuwa Bilkisu tana diney suna break fast da
dearest dinta sai ringing din wayarta taji, tashi tayi ta nufi saman kujera
inda wayar ke faman kara o wake kirana da sasssafen nan, dubawanda zatayi taga
Ummarta ce da sauri ta dauka salam alaikum umma ina kwana, lafiya ba wata
matsala umma, muna cikin koshin lafiya, Umma lafiya dai ko dariy atayi sanna tace
to ummah, amen,amen, amen umma mungode, zaiji ahan sai anjima ina gaida abba
sosai ummah, tau amen umma nagode, to sai anjima aha, ta katse wayar ta ajiyo
ko lafiya umma keta faman jeromata tambayoyi haka, wanna addu’a tasha bamaban
da irin addu’oin da umma keyi masu a kullum, sauri tayi ta kore wanna tunani ta
koma dany, wayene? Sulaiman ya tambaya, umm ace tace tana gaida kai Allah sarki
ina ansawa lafiya take dai ko lafiya kalau take bilkisu ta amsa, ya mutan gidan
ina fatan kowa lafiya ko? Kowa lafiya kalau madallah, please in kunji waya ina
gaidasu koda yake idan ma naje office inada niyar na kirasu, mikewa yayi ya
shiga daki ya dauko mukullin mashin dinshi ya fito bari na wuce to karna makara
har kofar gida bilkisu ta rakashi, koda yake tai iyyar ta bude gate din cewa
kawai yayi ta rike mashi, bayan ya fitada mashin din kuma ya dawo ya rufe da
kanshi wai shin baya son ta wahala ita dai dariya kawai takeyi tad an rakashi
waje, ai kinfita yayi can I have a pot? Ya tambaya yana yar kasha murya dariya
tayi tace no langabewa yayi kamar mai shirin kuka please don Allah, fashewa
tayi da dariya yadda taga yayi said a tasa hannu daya ta rufemai idanu sannan
ta yimasa kiss a kumatu, wani dogon ajiya zuciya yayi thanks a lot matata kin
biya yanzu zanje office da karfi suka fasa dariya su duka ya fito da nufin hawa
mashin dinshi ita kuwa tana bayanshi wani tsoho sukeyi kicibis dashi zaune a
kusa da gidan su kanshi na duke ga dukan alamu yana neman taimako. Nauyin mutanen
da yaji yasa ya daga kanshi su Bilkisu ya gani suna kallonshi cike da tausayi
yauwan yaro don Allah ko da akwai abinda zaku taimakamin dashi wallahi ina
neman taimako, hannu Sulaiman yasa a aljihu ya zaro dari biyar ya bashi ga
wannan da hanzari ya karba nawa zan shire dauka nab aka baba, dauka! Nagode,
nagode Allah ya saka da alkhairi Allaah ya biyaka amen kawai Sulaiman yace yah
au mashin, har ya tada mashin din Bilkisu tace mashi bari na kawo mishi sauran
break fast dinmu, yauwa jeki kawo masa ya tada mashin ya wuce, ita kuwa Bilkisu
ta shiga gida ta zuba masa ragowar abincin da sukaci ta fito waje ta kawo masa,
nagode, nadoge Allah ya biyaki, Allah yak are ku daga sherin duk wani mai
sharri, gaskiya kunada hankali da nutsuwa kun dace sosai, kinyi dacen miji,
shin kuwa yayi dacen mata, allah ya barku tare ya baku zuri’a dayyiba, murmushi
tayi tace amen, har a ranta taji dadin kalaman shon nan ta shige gida ta rufe
kofa. Wai Bilkisu yau har wanka nawa zakiyi ne Sulaiman ya tambayi Bilkisu wadda
take ta faman goge jiki da tawel, dariya tayi, ko wanka nawa nayi dai-dai nike
ai, domin yanada kyau ga kowace matar aure ta kansance mai yawan wanka tana
tsafface jikinta, domin (bad ordour) is natural wanan ga duk wani wanda
shekarunsa suka kai, ba ko a son duk
wata macen aure mijinta ya shaki wannan smell din, (adressing mirrow) ta zauna
bayan kamala jawabinta, hakane your bighness sulaiman yace tareda mikewa akan
gado ya bude, bandaki ya shiga, guntun murmushi tayi ta zaro (comp) ta fara
shace kanta, zara comp din ta sakeyi a gashinta me zata gani!! Ga baki dayan
inda ta shace duka gashinta ya cire saura ya fadi kasa sura kuwa yana a jikin
comp din, kamar dai wadda ta saka (cliffer) ta aske wurin haka wurin yayi,
wurgi tayi da (comp) din ta mike tsaye ta fara ja da baya tana kallon taswirar
ta a cikin dressing mirrow din, ga baki daya gashin saman kanta zubewa yakeyi
yana yankewa daga lokacin duka gashin ya zube cikin kankanin lokaci, ba suma ko
daya kamar wadda tayi aski da rega. Wata irin karat a buga mai tsanani karfi, a
guje Sulaiman ya fito daga cikin bandaki, ga baki daya ta fita hayyacinta, gam
yariketa Bilkisu lafiya! Bilkisu! Sumana! Sumana! Kawai take kira, me ya faru
da sumanki nuna masa mudubin tayi dad an yatsa, me sumanki tayi kai hannu yayi
ya taba sumanta, dai-dai lokacinda ta kai dubanta ya zuwa madubi, me zata gani
kuma!! Sumanta dai yananan kalau ba abinda ya sameshi, cak ta tsaya kamar
abinda aka zarewa lakka, baya-baya ta ringa ti shi kuwa Sulaiman yana riketa
tama rasa ta inda zata fara, wasu zafafan hawaye suka rika zubowa takan
kumatunta, kuka takeyi baji bagani gabaki daya al’amarin gidanan ya isheta
wannan wace irin rayuwace mai dauke da firgici da tashin hankali, a hakikanin
gaskiya dab a domin tana yiwa Sullaiman HUBBIL YAKIN bad a ba abinda zai hana
ta gudu ta koma garinsu ko zata tsira daga wannan ukuba, Sulaiman ya shiga
aikin sa rarrashin ta ya ringa yi tareda yimata nasifa akan komai yayi tsanani
saukin na nan zuwa, a haka suka kwana kowa da abinda yake sakawa a nashi ran ka
shegari Bilkisu tayi kokarin ta sharar da abinda ya faru da dare bayan sunyi
break fast tar aka mijinta kamar kullum, fitarsu keda wuya suka yi kicibis da
tsohonnan da suka saba taimakawa a kwanakin baya. Gaidashi sukayi da yar
fara’ar su, da hanzari ya amsa shima yana mai nuna fara’arshi a fili kamar
wanda ya dade da sanin su, wannan karon ma Sulaiman dari biyar ya bashi yah au
mashin dinshi yayi gaba, ita kuwa Bilkisu taje ta zuba mashi ragowar abinci,
yayi sallama yawuce sannu a hankali suka fara sabawa das hi, har y azan idan ya
dade bai zo ba, daga bisani ya zo sukan tambayi dalili. Sun shaku matuka da
juna har sunayimasa kallo a matsayin dan uwan shima kuwa yana yi masu kallon
diya. Bilkisu ce zaune a falo taci wanka harta gaji tana kallo, sallama taji
ana rangada wa, da hanzari taje ta bude kofa su Fatima ne suka kawo mata ziyara
taje ta bude kofa sannunku da zuwa ku iso. Makotan ta ne su Khadija da Fatima
suka kawo mata ziyara. Sannun ku fad a zuwa ku zauna, taje ta kawwo musu
abinsha ta ajiye musu, ta nemi gu itama ta zauna, bayan sun dan karba abinda ta
kawo musu Fatiman ta fara da cewa Amarya bakya laifi ko kin kasha yar masu gida
murmushi kawai tayi rufamin asiri ta fada wanna kwalliya haka ai sai ki hana
angon ki fita waje, wannan karon dariya tayi ni dai don Allah kurufamin asiri.
I fira suka ringayi da juna abin gwanin ban dariya, gaskiya su Fatima akwaisu
da raha abinda ya dauke hankalinsu daga firar da sukeyi wani film dinda akayi
na india mai suna Ghajini film din yayi kyau sosai. Sun dan dade suna fira
kafin Khadija ta daga kai ta kai dubanta ya zuwa wani karon inlargement na
Bilkisu da mijinta Sulaiman a lokacin aurensu, Wow!! Masha allah! Ta fada
batareda tasan a baiyane ta fada ba tsananin kam da sukayi yadda suka yi kama
da juna baka sai kace ‘yan biyu, agaskiya sunada kama sosai da mijinta kuma ba
kananan indiyawa bane wajen kyau, su duka sun yaba da kyan ilargement din tare
da fatan ganin yadda ya yansu zasu kasance ta fannin kyau. Ita dai Bilkisu bata
samu ta cewa ba kyalesu tayi sukayi ta zuba abinsu sai da suka tashi zasu wuce
Bilkisu ta rakasu kamar wadda ta tunada wani abu da hanzari ta tambayesu, ina
ake kitso nan unguwar don Allah? Me kike nufi? badai tunda kikazo maigidan keyi
miki kitso ba Fatima ta fada suka bushed a dariya ga baki dayansu. A’a wata yar
office dinsu yake kaini gidanta takemin to bata iya irin wanda nake so ba wibin
kawai ta iya kullum abin daya mukeyi abin duk ya fara isata. Anan bayan mu kuwa
akwai wata inna Kande ko wane irin kitso kike so ta iya, amma da wuya ki gane
gidan daga kwatance idan dai kika tashi kibiyo ta gidanmu ma hadaki da Habiba
yar aikin mu sai ta kai ki. To ni ko gobe ma ba sai tazo ta kaini koda yake ba
sai kinzo ba ma aikota goben ta kaiki. Kin san halinmu da surutu kar kizo mu
tsaidaki. Dariya tayi tace ina jira har garka tar aka su sukayi bankwana suka
wuce ita kuwa ta dawo daga cikin tana dariya.
No comments:
Post a Comment