Garabasa
Farin cikin
zuciya ta
Assalamu
alaikum,
Ya ke farin
cikin zuciya ta kuma sanyi idanuwa, hakika ke cewa face ta farko wacce na yi
gamu da ita, bantaba zato ko tsammani ba za’ayi wata ‘ya mace wacce zata sace
min dukkanin ruhi a mafi kankantar lokaci ba, amma sai gashi ba tsammani nayi
kicibis da kyakkyawar muskar da na kasa dauke wa kallo.
Hakika tun
lokacin da idaniya ta kalle ki zuciya ta kamu da ciwon sonki, na aiko miki
wannan sako ne ba don komai ba sai don na rasa irin hanyar da ya dace na biyo
kwana da kwanaki ina tunani da irin hanyar da zan biyo ta sanar da ke wannan
cutar da Allah ya yi min jarabawa da ita, amma ina, na kasa na yi tunanin samun
ki a makaranta domin na sanar da ke irin kaunar ki da ke kunshe a cikin zuciya,
sai naga ba mafi sauki irin rubutu miki wannan wasikar.
Ka da na cikaki
da surutu ya ke hasken zuciya ta kin riga kin zamu ginshikin rayuwata, ina
sonki, ina kuma kaunarki, a kullun ke ce abin tunane na, zan rasa dukkanin
farin ciki idan har ban samu amincewar ki ba, hakika zuciya zata dan dani wata
irin azaba idan kika ce bakya tare da ni.
Daga karshe ina
miki fatan alkhairi, ina kuma sauraru daga gareki, nagode.
Masoyin ki na har abada
Ahmad Muhammad Kabir
No comments:
Post a Comment