Saturday, 31 March 2018

Wasikon Soyayya Series 2


Na shiga tsaka mai wuya
Salam, barka da wara haka ina fatan aminin zuciya a mafi ribatuwar rayuwa, bayan haka; ya kai sanyi idanu na sani kai na a mafi munin safiya yau ne ranar da bazan taba mantawa da ita ba, kuma yau na dauki biro na rubuta a kundin tarihin rayuwata.

Aminin zuciya ina baka hakuri dangade da abin da ya faro nasan nayi kuskure kuma abinda nayi ban kyautaba, hakika shedan ne sanadiyar afkuwar wannan al’amari.

Masoyina!, idan baka hakura ba shin wa zan nemi afuwa gunsa? Kada ka manta kai kadai ne farin cikin rayuwata kuma kai ne wanda nake fata ka zame man sanyi idanu na. ina sahibin zuciya? Ahmad ina sanar da kai cewa na dauki alkawari ba wani abin da zai sa in dai na kaunar ka, Kaunar ka ce kadai a zuciya ta, kuma kai ne Insha Allahu wand azan zamo mata a gareshi.
Ina sonka Ahmad
Daga Sahibar ka
Zainab Isma’ila


No comments:

Post a Comment